Connect with us

News

Kotu Ta Sake Haramta Wa VIO Kama Masu Ababen Hawa 

Published

on

Kotu ta dakatar da hukumar VIO daga cin tarar masu ababen hawa a Najeriya

Kotun Daukaka Kara ta Abuja ta tabbatar da hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta yanke, wanda ya haramta wa Hukumar kula da lafiyar Ababen hawa (VIO) ikon dakatar da motocin jama’a, kwace su ko kuma kakaba tara.

Kotun ta kuma bada umarnin biyan N1 miliyan ga direban Abuja, Abubakar Marshal, wanda ya kai karar.

Advertisement

K-MAN Ta Taya Christopher Musa Murnar Rantsar da Shi a Matsayin Ministan Tsaro

A hukuncin da aka fara yanke wa a ranar 2 ga Oktoba, 2024, Mai Shari’a Nkeonye Evelyn Maha ta bayyana cewa babu wata doka da ke bai wa VIO ikon tilasta bin dokokin zirga-zirga.

Shari’ar ta samo asali ne daga korafin da lauyan kare hakin dan adam, Marshal, ya shigar, inda ya kalubalanci abin da ya kira cin zarafin ’yan Najeriya da VIO ke yi.

Advertisement

Kotun ta kuma bayyana cewa wannan hukunci bai shafi FRSC ba, wadda ita ce hukumar da doka ta amince da ita wajen aiwatar da dokokin zirga-zirga, tare da bayar da umarnin hana VIO ci gaba da tsoma baki ba bisa ka’ida ba.

 

Advertisement

 

DAILY NIGERIAN

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending