Connect with us

News

‎’Yan Rakiyar Amarya 14 Sun Mutu Sakamakon Kifewar Wani Jirgin Ruwa A Kebbi ‎

Published

on

boat mishap 768x538.jpg

Aƙalla mutane 14 ne suka rasa rayukansu sakamakon kifewar wani jirgin ruwa a kogin River Niger da ke yankin Gumbi, cikin karamar hukumar Yauri dake jihar Kebbi , a arewa maso yammacin Najeriya.

‎Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mutanen da hatsarin ya rutsa da su na cikin tawagar da ke rakiyar wata amarya zuwa gidan mijinta a Gwarzo, cikin karamar hukumar Ngaski , lokacin da jirgin ruwan ya kife.

Advertisement

Malam Sulaiman Marafa Ya Karɓi Aiki A Matsayin Manajan Filin Jirgin Sama Na FAAN A  Gombe

‎Shugaban karamar hukumar Yauri, Abubakar Shu’aibu, ya bayyana cewa sama da mutane 100 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

Advertisement

‎Ya ce zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 14, ciki har da mata 13 da kuma karamin yaro guda.

‎A cewarsa, an riga an binne dukkan mamatan bisa ka’idojin addinin Musulunci.

Advertisement

‎Gwamnan jihar, Nasir Idris, ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu da al’ummar masarautar Yauri, yana mai kira gare su da su karbi wannan ibtila’i a matsayin kaddara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending