Connect with us

News

Keir Starmer Ya Yi Murabus Daga Mukamin Firaministan Birtaniya

Published

on

FB IMG 1782120038586

Firaministan Birtaniya Kier Starmer ya sanar da murabus daga muƙaminsa, kodayake ya ce zai ci gaba da zama kan kujerar har zuwa lokacin da jam’iyyar Labour za ta yi zaɓen sabon jagora wanda zai zama magajinsa.

Da safiyar yau Litinin ne Starmer ya sanar da wannan mataki yayin wani taro da ya kira a harabar Downing Street, gaban idon manyan muƙarraban gwamnatinsa tare da manema labarai.

Advertisement

Wasu Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Cikin jawabinsa, Firaministan na Birtaniya mai murabus, ya ce nan da watan Satumba ne za a gudanar da zaɓen sabon jagora don jan ragamar ƙasar, sai dai kafin nan zai ci gaba da aiki a matsayin mai barin gado.

Advertisement

Cikin yanayi na shessheƙar kuka ne Keir Starmer ya tabbatar da wannan murabus inda ya ce zai haƙura da kowanne aiki tare da mayar da hankali wajen baiwa kyakkyawar matar shi da yaranshi kulawar da ta kamata.

Murabus ɗin na Starmer kai tsaye ya buɗe ƙofa ga Firaminista na 7 cikin shekaru 10 a ƙasar, wadda ta faɗa cikin rikicin siyasa tun bayan ficewa daga ƙungiyar Tarayyar Turai.

Advertisement

Tsawon watanni Starmer ya shafe yana fuskantar matsin lamba tare da neman murabus ɗinsa, sai dai lamarin ya fi tsananta a yanzu tun bayan da Andy Burnham ya lashe zaɓe tare da dawowa Westminster.

Ƙasa da shekaru 2 baya ne Starmer ya lashe zaɓen ƙasar tare da alwashin daidaita matsalolin siyasar da suka dabaibaye ƙasar.

Advertisement

 

 

Advertisement

RFI

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending