News
Gwamnatin Tarrayya Ta Sanar Da Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Oyo
Gwamnatin Najeriya ta sanar da ceto ɗalibai da malamansu da aka sace a makarantu uku na jihar Oyo ta kudancin Najeriya, fiye da kwanaki 50 da yin garkuwa dasu yau.
Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaba Tinubu ne ya sanar da haka yau Jumma’a, inda ya ce jami’an tsaron ƙasar ne suka ceto su daga hannun ƴan ta’adda.
A ranar 15 ga watan Mayun da ya gabata ne, ƴan bindiga suka sace ɗalibai da malamai 46 cikin har da shugaban makaranta daga makarantun yankin Ogbomosho da ke jihar Oyo.
Kwanaki bayan harin, ƴan bindigar suka fitar da wani faifan bidiyo da ke nuna yadda suka yiwa wani malamin lissafi na guda cikin makarantun, Michael Oyedokun yankan rago, lamarin da ya haifar da zazzafar muhara.
Bayan hakan ne kuma, ƙungiyar malamai na NUT da sauran masu ruwa da tsaki suka gudanar da zanga-zanga don nunawa gwamnati fushinsu.
Haka zalika, matsin lamba ya gwamnati ya tsananta bayan fitar wani bidiyon Mrs Rachael Alamu, shugabar makarantar sakadire ta Ahoro-Esiele, inda ta ke roƙon mahukunta su gaggauta ceto su.
Sace ɗaliban dai ya ƙara janyowa gwamnatin Najeriya baƙin jini, kasancewar acan jihar Borno ma a rana guda aka sace wasu ɗalibai a Askira-Uba, abinda ya sake fito da irin yadda matsalar garkuwa da mutane ke neman zama ruwan dare a sassan ƙasar.
-
News3 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News4 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News4 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
