News
An Kama ’Yan Ƙasar Waje Biyu Kan Zargin Shirya Garkuwa Da Mutum A Kwara
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kwara ta tabbatar da kama wasu ’yan ƙasar Togo biyu da ake zargi da shirya yin garkuwa da wani mazaunin jihar tare da neman kuɗin fansa har Naira miliyan 22.
Mai magana da yawun rundunar, SP Adetoun Ejire Adeyemi, ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce waɗanda ake zargin sun yi wa mutumin barazanar cewa za su yi garkuwa da shi tare da kashe ƙaninsa idan bai biya kuɗin da suka nema ba.
Kotu Ta Haramtawa Jami’an FRSC (Road Safety) Tare Motoci A Titunan Kano
A cewarta, bayan samun sahihan bayanan sirri, jami’an rundunar suka gudanar da bincike, lamarin da ya kai ga cafke mutanen biyu tare da ƙwato wata wayar salula da ake zargin an yi amfani da ita wajen yin kiran barazanar.
SP Adeyemi ta ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun amsa suna da hannu a wannan shiri.
Ta ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano tare da cafke sauran waɗanda ake zargin suna da alaƙa da lamarin, kafin gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar hukunci.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
