News
Ademola Ya Sake Lashe Zaben Gwamnan Osun
Hukumar zabe ta Najeriya INEC ta ayyana Ademola Adeleke na jam’iyyar Accord Party a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jihar Osun da aka gudanar ranar Asabar.
Advertisements
Advertisements
Adeleke ya samu nasarar lashe wa’adi na biyu ne bayan da ya doke babban abokin hamayyarsa, Bola Oyebamiji na jam’iyyar APC.
Advertisements
Jama’a Sun Yi Cirko-Cirko Domin Dibar Ganimar Man Da Tankar Mai Ta Zubar
Advertisements
Advertisements
Jami’in tattara sakamakon zaben, Joshua Ogunwole, ne ya sanar da sakamakon a cibiyar tattara sakamakon zaben INEC da ke Osogbo a safiyar Lahadi.
A cewarsa, Adeleke ya samu kuri’u 511,067, yayin da Oyebamiji na APC ya zo na biyu da kuri’u 444,815. Najeem Salaam na jam’iyyar ADC kuma ya zo na uku da kuri’u 17,180.
Advertisements
