News
Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Manyan Sakatarori 3 Kan Gano Hukumar Bogi
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin kama wani mutum, Prince George Buchi Nwabueze, bisa zargin hannu wajen kafa wata hukumar bogi a Abuja.
Haka kuma, Shugaban Ƙasar ya dakatar da manyan sakatarori uku a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) dangane da lamarin.
FBI Ta Ce Ba Za Ta Iya Sakin Wasu Bayanan Binciken Shugaba Tinubu Ba
Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa Mai Zaman Kanta (ICPC), Dokta Musa Adamu Aliyu, SAN, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan ganawarsa da Shugaban Ƙasa ranar Juma’a.
Ya ce an gano wata hukuma mai suna Ofishin Ayyuka na Musamman na Ƙasa, wadda aka kafa ba bisa ƙa’ida ba, a cikin harabar Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Manyan sakatarorin da aka dakatar su ne M.S. Danjuma, Injiniya Nadungu Gagare da Richard P. Pheelangwah.
A cewar shugaban ICPC, an gano hukumar ta bogi ne yayin binciken da hukumar ke yi kan wata ƙungiya da ake zargi da kasancewa ta bogi, mai suna Majalisar Tallafawa Harkokin Waje ta Shugaban Ƙasa, wadda Adeyemi Matthew ke gudanarwa.
Dokta Aliyu ya ce binciken ya nuna cewa an bai wa sabuwar hukumar ta bogi ofishi a cikin harabar Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, duk da cewa ba ta da hurumin gudanar da ayyukan gwamnati.
Ya ce umarnin Shugaban Ƙasa na kama Nwabueze da dakatar da manyan sakatarorin na daga cikin matakan da aka ɗauka domin zurfafa bincike kan lamarin da kuma gano sauran mutanen da ke da hannu.
ICPC ta ce za ta ci gaba da bincike domin tabbatar da cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin ya fuskanci matakin da ya dace.
-
News7 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized2 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
