Connect with us

News

Gwamnonin Najeriya za su ɗaukaka ƙara kan ƙayyade kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

Published

on

 

 

Kungiyar gwamnonin Najeriya ta ce za ta ɗaukaka ƙara game da hukuncin wata babbar kotu da ya kori ƙarar da suka shiga suna ƙalubalantar matakin da sashen tattara bayanan sirri kan hada-hadar kuɗi na ƙayyaɗe kuɗaɗen da ƙananan hukumomi za su rika kashewa a kullum.

Gwamnan Anambra Ya Sanya Dokar Hana Fita A Kananan Hukumomin Jihar 7

Babbar kotun ta ce gwamnonin ba su da hurumin hana kayyade naira dubu 500,000 a matsayin kuɗaɗen da ƙananan hukumomi za su rika kashewa a kullum ba.

Abdulrazak Bello Barkindo daraktan yaɗa labarai na ƙungiyar ya ce duk da cewa taron da gwamnonin suka shirya ranar Laraba bai yiwu ba, amma an cimma matsayar ɗaukaka ƙara kan hukuncin babbar kotun.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending