Politics
2023: Atiku zai zabi abokin takara ran talata, yayin da Tinubu ke shirin zabar musulmi ko Christa
Daga kabiru basiru fulatan
Hukumar zabe ta Najeriya, INEC ta bayyana cewa ba zata karawa jam’iyyu lokacin da zasu gabatar mata sunayen ‘yan takara da mataimakan su ba,
NAJERIYA A YAU: Shekara 23 Da Mulkin Dimokuradiyya: Ina Aka Kwana?
Wanda hakan yasa suma jam’iyyun suke kokarin ganin cewa sun gabatar mata dasu kafin wa’adin ya cika ranar 17 ga watan yuni watau juma’a mai zuwa.
Inda PDP ta shirya gudanar da gagarumin taro ranar talata da gwamnoni da sauran manyan jam’iyyar don zabarwa Atiku mataimakin da zai sa su lashe zaben 2023.
Yayin da jam’iyyar mulki ta APC ke shirin zabar musulmi a matsayin mataimakin Tinubu domin basu da wani kirista mai karfi sosai da ka iya sa jam’iyyar tayi nasarar lashe zaben 2023.
PDP na shirin zabar daya daga cikin Nyesom Wike ko kuma Udom
Yayin da APC ke shirin zabar Gwabna LaLong, Yakubu Dogara. Boss Mustapha, da Babachir,
A cikin musulmi kuma Zulum, Shettima, Ganduji, Bagudu,Badaru, da
El Rufa’i
Hakazalika
Na zaɓi wanda zai yi mini mataimaki, sunan sa na nan a ƴar takarda a gaban aljihuna na cakale
–Inji Tinubu
Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Tinubu ya bayyana wa manema labarai cewa tuni a ya ɓi wanda zai yi masa takarar shugaban kasa, kuma sunan wanda ya zaɓa na cikin yar takardar sa a gaban aljihu.
” Ƴanci na ne, kuma tuni na zaɓi wanda zai yi min mataimakin shugaban kasa, sunan sa na killace a cikin ƴar takarda ta da na cakale a gaban aljihuna.
Bayan haka Tinubu ya kara da cewa shi mutum ne mai dattaku da sanin ya kamata sannan ya na da kamala da kuma kwarewa a harkar shugabanci da da bunƙasa tattalin arziki.
Aiki ne a gaban mu, Tinubu ga APC
Ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga ƴan jam’iyyar su ɗaura ɗamarar yaki domin jan aiki ne a gaban su.
Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa ranar Alhamis bayan sunsa labule da Shugaba Bahari a fadar shugaban Kasa
Idan ba a manta ba Tinubu ne ya yi nasara a zaɓen fidda gwani na takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC wanda aka yi ranar Litinin zuwa Larabar wannan mako.
Ya lallasa yan takara 14 da suka gobza da shi a zaɓen.
Tsohon ministan Sufuri, Rotimi Amaechi ne ya zo na biyu a zaɓen inda mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya zo na uku a zaben.
Tinubu ya ziyarci shugaban kasa Muhammadu Buhari domin yi masa godiya da damar da ya baiwa duka ƴan takara su gobza a tsakanin su ba tare da ya saka baki ba.
” Ina yin kira ga ƴan jam’iyyar mu ta APC da su zo mu haɗa hannu gaba ɗayan mu domin samun nasara a babban zaɓe.
” Shugaba Muhammadu Buhari ya yi abinda ya dace a wannan zaɓe na fidda gwani. Da ma kuma ya yi alkawarin ba zai sa baki ba a zaɓen kuma ya cika alkawarin sa.
” Yanzu jan aiki ne a gaban mu. Cin babban zaɓe shine ya kamata mu maida hankali a kai yanzu.
