Connect with us

Politics

Yakamata APC Ta Baiwa Arewa Mason Gabas Mukamin Mataimakin Shugaban Kasa Domin Kada Atiku A Zabe—– Matasan APC

Published

on

Daga Muslim yunus Abdullah 

 

Advertisement

 

Kungiyar matasa masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a shiyyar arewa maso gabas ta yi kira ga jam’iyyar APC da ta Mika mataimakin shugaban kasa ga yankin.

Advertisement

Darwin Nunez: Liverpool ta kulla yarjejeniya da Benfica kan dan kasar Uruguay

Shugaban kungiyar, Haruna Sardauna ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai jiya a Abuja.

Advertisement

 

Kungiyar ta yi nuni da cewa, maida matsayin yankin Arewa maso gabas zai kawar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, wanda ya fito daga yankin.

Advertisement

 

Ta ce, “Mika mataimakin shugaban kasa zuwa Arewa maso Gabas zai kawar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP tare da samar da gagarumin goyon baya daga yankin da sauran shiyyoyin domin tabbatar da nasarar Alhaji Ahmed Bola Tinubu.

Advertisement

 

Kungiyar ta yi nuni da cewa duk wanda aka zaba daga yankin, musulmi ne ko Kirista zai tallafa musu.

Advertisement

 

Ya kara da cewa shiyyar Arewa maso gabas ta kasance tana baiwa jam’iyyar APC kuri’u tare da goyon bayan ‘yan takara daga yankin tun daga farko.

Advertisement

 

Kungiyar ta dage cewa ya kamata a duba yankin Arewa maso Gabas duba da irin sadaukarwar da yankin ya yi wa jam’iyyar ta APC Mai mulki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending