News
PDP ta kafa kwamitin nemo wa Atiku mataimaki
Daga Maryam bashir musa
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta kafa kwamitin da zai yi aikin nemo wa dan takararta na shugaban kasa, Atiku Abubakar, mataimaki.
Ba masu juya gwamnati ne ke sa ni daukar matakan siyasa ba – Buhari
Makonnin da suka wuce ne tsohon mataimakin shugaban kasar ya lashe zaben fid da gwani, a matsayin wanda zai yi wa PDP takara a babban zaben 2023.
Shugaban jam’iyyar Sanata Iyorchia Ayu ne ya kaddamar da kwamitin a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja ranar Talata.
Mataimakin Shugaban jam’iyyar shiyyar Arewaci Ambasada Umar Damagum ne zai jagoranci kwamitin, a daidai lokacin da hukumar zabe wato INEC ke dakon a mika mata sunayen ‘yan takarar shugaban kasa da mataimaki a kwanaki masu zuwa.
Masu sharhin siyasa na ganin Atiku Abubakar, wanda ya fito daga Arewacin kasar, zai dauko mataimaki ne daga Kudanci, la’akari da yadda fasalin Najeriya yake.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
