Connect with us

News

Ba masu juya gwamnati ne ke sa ni daukar matakan siyasa ba – Buhari

Published

on

Daga yasir sani Abdullah 

 

 

 

Fadar Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ta fitar da sanarwar da ke cewa shugaban na daukar matakan siyasa a kashin kansa, ba tare da katsalandan daga mutanen da ake tunanin suna juya gwamnati ta bayan fage ba ake kira ‘Cabal’.

KISAN HANIFA: Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Ranar 28 Ga Yulida

Advertisement

 

Sanarwar na dauke ne da sa hannun mataimaki na musamman ga shugaba kan yada labarai Malam Garba Shehu.

 

Wani bangare na sanarwar ya ce ”Shugaba Buhari na daukar matakansa ne kuma ya aiwatar da su ba tare da tsoma baki daga wasu wai su ‘cabal’ ko wasu masu uwa a bakin murhu ba.”

 

Sanarwar na zuwa ne bayan jita-jitar da ke yawo a kafafen yada labarai da ke cewa shugaban ne ya yi uwa da makarbiya wurin zaben fid da gwani da aka yi kwanakin baya, da ya samar da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC.

Advertisement

 

Haka kuma ta ce irin yadda aka gudanar da zabe fid da gwani na dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC ya nuna cewa Shugaba Buhari ba mai mulkin kama-karya ba ne.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending