Dan takarar shugabancin Najeriya na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar, ya ce suna daukar matakin wajen yin sulhu da mutanen da aka batawa a jam’iyyar.
- An sace ‘yan China da kashe jami’an tsaro a jihar Neja
- Jarumar Fina-finan Ta Nollywood Sun Rabu Da Mijinta.
A wasu jerin sakonni da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Alhamis, tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce yana kaunar kowanne dan jam’iyyar, cikinsu har da gwamnoni.
“Peoples Democratic Party (PDP) za ta ci gaba da kasance a dunkule. Ku mayar da hankali kan matakan da muke dauka. Muna daukar matakai domin shawo kan korafin kowa,” a cewarsa.
“Hadin kan jam’iyyarmu shi ne babban abin da na sanya a gaba. Matakin farko na hadin kan Najeriya zai soma ne daga jam’iyyarmu zuwa cikin al’umma,” in ji Atiku Abubakar.
