News
Mutuwar Dr. Ahmad babban giɓi ne a duniyar ilimin Hadisi – Atiku

Daga muhammad muhammad zahraddin
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa saƙon ta’aziyyar rasuwar babban malamin addinin nan na Kano, Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, wanda a ka fi sani da Kala Haddasana wanda ya rasu a jiya Juma’a.
Atiku wanda ya wallafa sakon ta’aziyyar a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a ya ce, ya yi matuƙar kaduwa lokacin da ya samu labarin rasuwar Dr. Ahmad.
“Na kaɗu matuƙa da samun labarin rasuwar Dr. Ahmad Ibrahim Bamba”.
“Rasuwar Shehin Malamin ya bar babban giɓi a duniyar ilimin Hadisi wanda zai yi wahalar cikewa.
“Mutuwar sa babban rashi ne ga duniyar Ilimin Hadith da sauran rassan Ilman Musulunci. Ya sadaukar da dukkan rayuwarsa wajen ilmantarwa da wayar da kan mutane. Haƙiƙa an saurari karatuttukansa a dukkan sassan duniya”.
“Ina addu’ar Allah ya ji ƙan sa sannan ya bai wa iyalai da abokansa haƙurin rashinsa. “Addu’ar Allah ya gafarta masa zunubansa, Ya haɗa shi da salihan bayi, ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus. Ameen”. In ji Atiku
Sheikh Dr. Ahmad ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano kamar yarda PlatinumPost ta ruwaito.