Connect with us

News

Ƴan bindiga sun kashe mutum 5 a Naija

Published

on

FB IMG 16425817289986699
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Naija ta tabbatar da kashe jami’an ta uku da kuma ƴan vigilante 2 a wani harin kwanton-ɓauna da ƴan ta’adda su ka kai musu a Kwanan Dutse, Ƙaramar Hukumar Mariga a jihar.

Advertisement

Kwamishinan Ƴan Sanda na jihar, Sunday Bala Kuryas ne ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Daillancin Labarai na Ƙasa, NAN ta wayar tarho.

Kuryas ya ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin da misalin ƙarfe 4 na yamma lokacin da jami’an tsaro na haɗin gwiwa su ke sintiri a yankin.

Sai dai kuma a cewar sa, su ma jami’an sun hallaka ƴan ta’adda da dama a bata-kashin da a ka dau lokaci a na fafatawa.

Ya kuma ƙara da cewa, ko a ranar Lahadi, sai da rundunar tsaron ta haɗin gwiwa ta daƙile wani yunƙurin kai hari bayan an kwashe awanni biyu ana fafatawa da ƴan ta’addan a ƙauyen Bari, kan titin Tegina-Kontagora.

Advertisement

Ya kuma kara da cewa tuni rundunar ƴan sanda, ɓangaren sintiri na musamman da sojoji sun fara bibiyar ƴan ta’addan domin tabbatar da kame su.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *