News
An kashe matar aure a cikin gidanta a Kano
Daga kabiru basiru fulatan
Mutanen unguwar Danbare da ke Ƙaramar Hukumar Gwale a Jihar Kano sun shiga tashin hankali da alhini bayan da a ka iske an kashe wata matar aure, mai suna Rukayya Mustapha a cikin gidan aurenta.
Jaridar indaranka ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a yammacin Asabar, inda makasan na Rukayya su ka kuma ji wa ƴaƴanta biyu ƙanana rauni.
Wannan jaridar ta kuma jiyo cewa an yi amfani da taɓarya ne a ka buga wa marigayiyar a kanta, inda ta ce ga garin ku nan.
Ba a san ya a ka yi makasan su ka shiga gidan ba duk da cewa, an ce a kwai wasu masu aikin gini a maƙotan gidan da abin ya faru.
An ce ba wanda ya san mai ya faru har sai da mijin ta ya dawo da ga kasuwa sannan ya tarar da ita a kwance ta mutu.
Da wakilin mu ya kira Kakakin Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, bai samu ya amsa wayar ba.
Sai dai kuma BBC Hausa ta rawaito cewa SP Kiyawa ya ce rundunar ta kama mutane biyar da a ke zargi da hannunsu a kisan.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
