News
Kotu ta yanke wa korarrun ƴan sanda 2 hukuncin kisa sakamakon yin fashi da makami
Daga aminu usman jibrin
A yau Alhamis ne Mai Shari’a Peter Kekemeke na Babbar Kotu a Abuja ya yanke wa wasu korarrun ƴan sanda guda biyu hukuncin kisa sakamakon aikata fashi da makami.
Waɗanda a ka yanke wa hukuncin su ne James Ejeh da Simeon Abraham.
An gurfanar da su je a gaban Alƙali a ranar 20 ga watan Oktoba, 2017 a bisa kaifuka biyu da su ka haɗa da haɗin baki da fashi da makami.
Da ya ke yanke hukunci, Kekemeke ya ce mai ƙara ya gamsar da kotu ba tare da wani haufi ba bayan ya kira shaidu huɗu.
Alƙalin ya ƙara da cewa shaidu da a ka gabatarwa kotun sun tabbatar da cewa waɗanda a ke ƙarar sun aikata fashi tare da makami a hannayensu.
Ya kuma ƙara da cewa sun amsa laifin na su kuma babu wata shaida sama da amsawar da su ka yi.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
