Kungiyar ɗalibai ta NANS a Najeriya ta ba gwamnatin tarayya da ƙungiyar malaman jami’a ASUU wa’adin mako ɗaya su sasanta ko kuma su fuskanci bore ɗalibai a sassan ƙasar.
Shugaban ƙungiyar ɗaliban na ƙasa Sunday Adedayo ne ya yi wannan gargadin a ranar Litinin a Sokoto, kamar yadda kafar talabijin ta Channels ta ruwaito.
Ya ce ƙungiyarsu ta yanke shawarar cewa idan har gwamnatin tarayya da ASUU suka kasa sasatawa zuwa Juma’a, “ɗaliban za su haɗa gangami da ba gwamnati yaren da za ta fahimta.”
“Mun tsayar da ranar 28 ga watan Fabrairu, dukkanin ɗaliban Najeriya da aka kora gida za su fito su rufe hanyoyin gwamnati da ofisoshin ma’aikatar limi da ta ƙwadago,” in ji shugaban ɗaliban
