Connect with us

News

Kotu ta yi watsi da karar neman hana wa Atiku tsayawa takara

Published

on

1645442520918
Spread the love

Daga muhammad muhammad zahraddin

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yi watsi da ƙarar da wata ƙungiya mai da’awar kare haƙƙin ɗan Adam ta shigar tana ƙalubalantar cancantar takarar tsohon shugaban Najeriya Atiku Abubakar.

Kungiyar mai suna Egalitarian Mission for Africa ce ta shigar da ƙarar tana ƙalubalantar cewa ba a Najeriya aka haifi Atiku ba, don haka ta ke neman kotu ta hana shi tsayawa takarar shugaban ƙasa.

Sai dai alƙalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ya yi watsi da ƙarar inda ya ce ba hurumin ƙungiyar ba ne, kamar yadda kamfanin dillacin labaran Najeriya NAN ya ruwaito.

Advertisement

Watsi da ƙarar na zuwa bayan gwamnantin Adamawa ta shaida wa Kotun cewa Atiku cikakken ɗan jihar ne wanda aka zaɓa gwamna a 1999, kuma ya zama mataimakin shugaban ƙasa daga 1999 zuwa 2007.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *