Connect with us

News

Nijar ta ga watan Shawwal, Najeriya kuwa sai Litinin za a yi Sallah

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ganin watan Shawwal, wanda ya kawo karshen watan azumin Ramadan a kasar.

Advertisements
Advertisements

Tuni dai Shugaba Mohamed Bazoum ya aike da sakon ‘Barka da Sallah’ ga ilahirin al’ummar kasar a shafinsa na Tuwita, inda ya yi addu’ar zaman lafiya da tsaro da hadin-kan kasar.

Wannan na zuwa bayan Najeriya, makwabciyar Nijar, ta sanar da cewa ba a ga watan ba tare da ayyana Litinin a matsayin ranar Sallah.

Kwamitin ba da shawara kan harkokin addini na Majalisar Sarkin Musulmi tare da hadin gwiwar kwamitin ganin wata na kasa ya ce bai samu wani rahoto daga kwamitoci daban-daban na kasar da ke tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal ba.

Advertisements
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending