Connect with us

Sports

Jesse Lingard Ya Raba Gari Da Manchester United

Published

on

Daga mujahid danlami garba 

 

Advertisement

 

Manchester United ta sake fitar da sanarwar raba gari da dan wasanta, Jesse Lingard, bayan kwantaraginsa ya kare da kungiyar.

Advertisement

 

 

Advertisement

Lingard, wanda ya shafe kakar wasanni ta bara a kungiyar kwallon kafa ta West Ham a matsayin aro dai ya gaza katabus a Manchester United a bana.

 

Advertisement

 

Dan wasan wanda dan asalin Ingila ne ya bi sahun Paul Pogba, na jerin ‘yan wasan da suka yi sallama da kungiyar.

Advertisement

 

 

Advertisement

Sanarwar ta ce “Manchester United ta tabbatar da Jesse Lingard zai bar kungiyar a karshen watan Yuni, idan kwantaraginsa ya kare.

 

Advertisement

 

“Muna amfani da wannan dama don gode wa Jesse kan yadda ya taimaki wannan kungiya a lokacin zamansa, muna masa fatan alheri a rayuwarsa ta gaba.”

Advertisement

 

 

Advertisement

A watan Janairu, Newcastle ta nuna sha’awar daukar dan wasan tsakiyar, amma Manchester United ta yi burus da tayin nata.

 

Advertisement

 

Kazalika, kungiyoyi kamar su AC Milan, Inter Milan, Juventus da kuma Atletico Madrid daga gasar Laliga sun nuna sha’awar daukar Jesse.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending