Sports
Jesse Lingard Ya Raba Gari Da Manchester United
Daga mujahid danlami garba
Manchester United ta sake fitar da sanarwar raba gari da dan wasanta, Jesse Lingard, bayan kwantaraginsa ya kare da kungiyar.
Lingard, wanda ya shafe kakar wasanni ta bara a kungiyar kwallon kafa ta West Ham a matsayin aro dai ya gaza katabus a Manchester United a bana.
Dan wasan wanda dan asalin Ingila ne ya bi sahun Paul Pogba, na jerin ‘yan wasan da suka yi sallama da kungiyar.
Sanarwar ta ce “Manchester United ta tabbatar da Jesse Lingard zai bar kungiyar a karshen watan Yuni, idan kwantaraginsa ya kare.
“Muna amfani da wannan dama don gode wa Jesse kan yadda ya taimaki wannan kungiya a lokacin zamansa, muna masa fatan alheri a rayuwarsa ta gaba.”
A watan Janairu, Newcastle ta nuna sha’awar daukar dan wasan tsakiyar, amma Manchester United ta yi burus da tayin nata.
Kazalika, kungiyoyi kamar su AC Milan, Inter Milan, Juventus da kuma Atletico Madrid daga gasar Laliga sun nuna sha’awar daukar Jesse.
-
News7 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News7 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
