News
Kotu a Legas ta yanke wa ɗan shekara 73 hukuncin zaman gidan yari na shekara 24
Daga maryam bashir Musa
Wata kotu a Jihar Legas ta yanke wa wani ɗan shekara 73 hukuncin zaman gidan yari na shekara 24 kan laifin almundahana.
Tun da farko hukumar EFCC da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ce ta gurfanar da shi a kotu kan zarge-zarge tara ciki har da batun bayar da cakin banki na bogi da satar miliyan 71.
Ana zarginsa ne da damfarar wani kamfani mai suna Nepal Oil and Gas Services Limited a wani ciniki da ya shafi sayar da wani fili a Onitsha da ke Jihar Anambra.
Advertisements
