News
ANA GAB DA FASALTA KUDIN TSARIN MULKIN LIBIYA
Daga Khadija Abdullahi Mahmud.
fara taron masu ruwa da tsaki don fasalta kundin tsarin mulkin kasar Libya da Masar ke jagoranta a birnin Cairo, a wani yunkuri na ganin an gudanar da zaben kasar da ta shafe shekaru ta na fama da rikici.
SOJOJIN FARANSA SUN CAFKE KWAMANDAN IS A SAHEL
Shiga tsakanin na Masar bisa jagorancin Majalisar Dinkin Duniya da aka faro a Lahadin da ta gabata, shi ne karo na 3 da ake gudanarwa a kokarin tabbatar da zaman lafiya a kasar da kuma gudanar da zabe.
Ana saran a shafe fiye da mako guda ana zaman tattaunawar wanda zai bayar da damar bibiyar kundin tsarin mulkin kasar da zai bayar da damar gudanar da zabe a kasar.
Taron ya kunshi mambobin majalisar Libya, da na babban kotun kasar da kuma bangarorin masu bayar da shawarwari baya ga kwararru daga bangarorin siyasa dukkaninsu bisa sanya idanun Majalisar Dinkin Duniya.
Babbar jami’Majalisar Dinkin Duniya da ke sanya idanu kan rikicin na Libya ya roki bangarorin da ke cikin tattaunawar su samar da gamsasshiyar matsaya da za ta kawo karshen rikicin siyasar kasar.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
