Connect with us

News

Ƴan bindiga sun harbe mutum 8 a wajen bikin suna

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kamfanin dillancin labarai na gwamnati, AIB, ya bayar da rahoton cewa, a yau Talata wasu ƴan bindiga suka kutsa kai wajen wani bikin suna tare da kashe mutane takwas a ƙauyen Sandiaba da ke lardin Koulpelogo da ke tsakiyar gabashin kasar Burkina Faso.

Advertisement

Maniyyata sun yi zanga-zanga a Kano bisa rashin samun kujerar zuwa aikin Hajji

AIB ta ruwaito cewa, wasu ƴan bindigan sun kutsa cikin kauyen Sandiaba da ke da nisan kilomita huɗu zuwa Soudoughin a lardin Koulpelogo a jiya Litinin.

Advertisement

 

Majiyar ta ce maharan sun kutsa kai cikin wani taron suna a cikin iyali, inda suka yi ta harbin kan mai-uwa-da-wabi, har su ka kashe mutane takwas.

Advertisement

 

A cewar AIB, har yanzu yanayin tsaro na ci gaba da haifar da damuwa a lardin Koulpelogo da ma wasu yankuna da dama a Burkina Faso, duk da matakan da jami’an tsaro ke ɗauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending