News
Ƴan bindiga sun harbe mutum 8 a wajen bikin suna
Daga kabiru basiru fulatan
Kamfanin dillancin labarai na gwamnati, AIB, ya bayar da rahoton cewa, a yau Talata wasu ƴan bindiga suka kutsa kai wajen wani bikin suna tare da kashe mutane takwas a ƙauyen Sandiaba da ke lardin Koulpelogo da ke tsakiyar gabashin kasar Burkina Faso.
Maniyyata sun yi zanga-zanga a Kano bisa rashin samun kujerar zuwa aikin Hajji
AIB ta ruwaito cewa, wasu ƴan bindigan sun kutsa cikin kauyen Sandiaba da ke da nisan kilomita huɗu zuwa Soudoughin a lardin Koulpelogo a jiya Litinin.
Majiyar ta ce maharan sun kutsa kai cikin wani taron suna a cikin iyali, inda suka yi ta harbin kan mai-uwa-da-wabi, har su ka kashe mutane takwas.
A cewar AIB, har yanzu yanayin tsaro na ci gaba da haifar da damuwa a lardin Koulpelogo da ma wasu yankuna da dama a Burkina Faso, duk da matakan da jami’an tsaro ke ɗauka.
