Connect with us

News

Hajjin bana: Ɗaya daga cikin alhazan Jihar Nassarawa ta rasu a Makka

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaban Hukumar Jin dadin alhazai ta Jihar Nasarawa, Mallam Idris Ahmad Almakura ya tabbatar da rasuwar Hajiya Aisha Ahmad, ɗaya daga cikin mahajjatan jihar da ke ƙasar Saudiya domin aikin Hajjin bana.

Ranar Juma’a za a ƙaddamar da Ƙur’anin da a ka fassara da yaren Igbo

Advertisement

Ya bayyana hakan ne a yau Laraba a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a birnin Makka.

 

Advertisement

A cewar Almakura, marigayiya Aisha, wacce ta fito daga Ƙaramar Hukumar Keffi a jihar Nasarawa, ta rasu ne bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya.

 

Advertisement

Shugaban Alhazan na Jihar Nasarawa ya bayyana cewa ta yi rashin lafiya kuma an garzaya da ita Asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah kafin ta rasu.

 

Advertisement

Kakakin hukumar, AbdulRazak ya shaidawa manema labarai cewa an yi jana’izar marigayiyar a makabartar Harami bayan sallar La’asar a jiya Talata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending