Connect with us

News

Al’umma a yawaita addu’a don samun zaman lafiya….Kwamared Hafiz Mustapha

Published

on

Kwamared Hafiz Mustapha

Daga yasir sani Abdullah 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Dan takarar majalisar dokokin Kano a karamar hukumar Gwarzo, Kwamared Hafiz Mustapha yayi kira ga al’umma dasu cigaba da yiwa kasar nan addu’a don samun zaman lafiya mai dorewa.

Kada a gajiya wajen yin addu’a don samun zaman lafiya-Hamisu Ibrahim chadari.

Advertisement

Hafiz Mustapha, wanda ke takara karkashin jam’iyar PRP yayi wannan kirane a sakon barka da sallah wanda mai taimakamasa na musamman kan kafofin yada labarai Aminu Abdullahi Ibrahim ya fitar a ranar Asabar.

Ya ce za samu saukin matsalar tsaron da kasar nan take ciki ne kawai ta hanyar addu’a tare da mika lamura ga Allah madaukakin sarki.

Advertisement

Ya kuma yi kira ga al’ummar Gwarzo da Getso dasu yi rijistar katin zabe domin kada kuri’un su a zaben 2023 dake tafe.

Kwamared Hafiz Mustapha, ya kuma ce ba zai baiwa al’ummar Gwarzo da Getso, kunya ba matukar suka zabe shi amatsayin dan majalisa dokokin jihar Kano.

Advertisement

Ya kuma yi fatan al’ummar jihar Kano zasu cigaba da shagulgulan sallah lafiya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending