News
Abinda ya sa muka hana zirga-zirgar Baburan Adaidaita Sahu cikin dare – Gwamnatin Kano
Daga kabiru basiru fulatan
Gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta hana zirga-zirgar baburan Adaidaita Sahu ne bayan samun shawarwarin hukumomin tsaro kan aikata laifuka da suka yi kamari cikin dare.
Shugaban hukumar KAROTA na jihar Kano Baffa Babba Dan Agundi ne ya bayyana hakan ga jaridar ‘The Historica Nigeria‘ da yammacin Litinin.
Gwamnatin APC Ta Jefa Najeriya Cikin Tsaka Mai Wuya — Kwankwaso
Ya ce matakin ya zama wajibi duba da wasu nau’ukan laifuka da suka zama ruwan dare a jihar Kano, wanda ake yin su da hadin kan wasu masu baburan Adaidaita Sahun.
Baffa Babba Dan Agundi na cewa, magance matsalolin ya zama wajibi don ci gaba da wanzar da zaman lafiya a tsakanin al’ummar jihar Kano.
‘Shakka babu laifin kwacen waya ya zama ruwan dare, wanda kowa ya tabbatar da hakan, haka zalika akwai laifuka da dama da ake amfani da babur din Adaidaita Sahu wajen aikatawa, wanda Gwamnati ta dauki gabarar magancewa’, shugaban hukumar KAROTA.
Baffa Babba Dan Agundi ya kuma bukaci masu gudanar da sana’ar Adaidaita Sahu da su baiwa GWamnatin Kano hadin kai, wajen wanzar da dokoki nagari, da za su taimaka wajen ci gaban jihar Kano.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
