News
Hausawan Sudan na zanga-zanga kan kisan ƴan uwansu
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
Al’umar Hausawa mazauna Sudan sun gudanar da zanga-zanga a biranen kasar da dama, domin nuna bacin ransu, game da kisan da aka yi wa ‘yan uwansu a rikicin kabilancin da ya barke ‘yan kwanakin nan a kasar.
Kotu Ta Janye Umarnin Hana Ganduje Karbo Bashin N10bn
BBC Hausa ta rawaito ta bakin Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa hukumomi sun ce mutum 79 ne aka kashe sakamakon rikicin na kabilanci tsakanin Hausawa da ‘yan kabilar Berti a jihar Blue Nile.
AFP ya ruwaito cewa daruruwan Hausawa ne suka fito zanga-zangar a Khartum birnin kasar rike da kwalayen da ke dauke da rutubun neman adalci ga ‘yan uwansu da aka kashe.
Advertisements
