News
Ƴan Nijeriya mazauna ƙasashen waje haziƙai ne ma su ilimi – Dabiri-Erewa
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
Hukumar kula da Ƴan ƙasa mazauna Ƙasashen Waje, NiDCOM, ta bayyana cewa ƴan Nijeriya mazauna ƙasashen ƙetare a matsayin waɗanda su ka fi kowa hankali da ilimi a Amurka da Birtaniya.
Shugabar hukumar, Abike Dabiri ce ta bayyana hakan ne a yau Laraba a Abuja, a wani taron manema labarai domin sanar da Bikin Ranar Mazauna Ƙasashen Waje na 2022.
An Tsinci Gawar Matashi A Cikin Kwata A Kano
An shirya gudanar da bikin ne a ranar 25 ga watan Yuli.
Taken bikin shi ne: “Hoɓɓasar Al’umma a Zamani a kan Kalubalen Ci gaban Ƙasa”.
Ta ce ƙwararru na ci gaba da masu kishin kasashen waje a fadin duniya sun yi nuni da cewa babu wata kasa a duniya da za ta ci gaba ba tare da taimakon al’ummarta mazauna ƙasashen waje ba.
A cewarta, ’yan kasashen waje sun kasance masu albarka ga kasarsu.
Don haka, ta ce, ƴan Najeriya mazauna kasashen waje su na ba da gudummawa sosai ga haɓɓakar tattalin arzikin ƙasar.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
