News
Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Wike A Fatakwal
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya gana da Gwamnan Jihar Ribas Nyesom Wike a Fatakwal.
Wakilinmu ya rawaito cewa, Sarkin ya gana da gwamnan ne a wata ziyarar ban girma da ya kai Fadar Gwamnatin Jihar a ranar Juma’a.
Gwamna Masari ya hana sayar da Shisha a Katsina
Ganawar tasu na zuwa ne a daidai lokacin da Sarkin Musulmin ya ziyarci babban birnin jihar domin bude taro Hadaddiyar Kungiyar Mata Musulmai ta kasa da aka yi a jihar.
Bayanai sun ce Sarkin Musulmin yana sauka a garin kai tsaye ya zarce gidan gwamnatin jihar inda suka shiga wata ganawa ta sirri
Advertisements
