Connect with us

News

NABTEB Ta Saki Sakamakon Jarrabawar NBC/NTC Na 2022

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar shirya jarrabawa ta NABTEB, ta saki sakamakon jarrabawar NBC da NTC na 2022 da aka rubuta.

 

Advertisement

Shugabar hukumar, Farfesa Ifeoma Isiugo-Abanihe ce ta sanar da hakan yayin taron manema labarai da suka shirya ranar Laraba a Benin.

Mun dinke barakar da ke tsakanin Tinubu da shugabannin APC na kasa – Bagudu

Advertisement

 

Da take jawabi ta bakin wakilinta kuma darakta a hukumar, Dokta Obinna Opara, ta ce mutum 87,668 ne suka rubuta jarrabawar a cibiyoyi 1,656 a fadin Najeriya da kasar Kwaddibuwa.

Advertisement

 

Farfesa Isiugo-Abanihe ta ce, lura da jimillar wadanda suka rubuta jarrabawar, an samu kari a yawan wadanda suka rubuta jarrabawar a 2021 da kashi 4.99 cikin 100.

Advertisement

 

Ta kara da cewa, mutum 58,569 (kashi 69.6 cikin 100) daga cikin wadanda suka rubuta jarrabawar sun samu makin ‘Credit’ darussa a akalla biyar, ciki har da Ingilishi da Lissafi.

Advertisement

 

Ta bayyana cewa duk da haka, kokarin da dalibai suka nuna a jarrabawar bara ya zarce na bana idan aka yi la’akari da yanayin darajar makin da suka samu.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending