Connect with us

Sports

Galatasaray na zawarcin Ronaldo, Kante na fuskantar rashin tabbas a Chelsea

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Galatasaray na son dauko ɗan wasan Portugal mai buga gaba Cristiano Ronaldo, mai shekara 37, daga Manchester United a watan Janairu. (Fotomac – in Turkish)

 

Advertisement

Babban jami’i a Bayern Munich Oliver Kahn ya ce kungiyar Bundesliga na duba yiwuwar sayo Ronaldo a sabuwar kaka.(Bild, via Mail)

Abin Da Kasafin Buhari Na Karshe Zai Kunsa

Advertisement

Wolves na sa ran tattaunawa da Julen Lopetegui a wannan makon, bayan da Sevilla ta kore shi a matsayin koci. (Sky Sports)

 

Advertisement

Ɗan wasan tsakiya a Faransa N’Golo Kante, mai shekara 31, na ganin Chelsea ba ta son tsawaita zamansa a kungiyar, a daidai lokacin da kwantiraginsa ke shirin karewa a sabuwar kaka. (Footmercato – in French)

 

Advertisement

Arsenal ta nuna zawarcinta kan ɗan wasan Porto da Iran mai shekara 30 mai buga gaba Mehdi Taremi. (A Bola, via TEAMtalk)

 

Advertisement

Real Madrid na farautar ɗan wasan Benfica mai shekara 18 asalin Portugal, Antonio Silva. (Calciomercato – in Italian)

 

Advertisement

Inter Milan na fatan cimma yarjejeniyar tsawo kan Calhanoglu bayan kungiyoyi ciki har da Everton sun gagara sayen ɗan wasan da ke buga tsakiya. (TEAMtalk)

 

Advertisement

Wani Attajirin Amurka Bill Foley, ya shiga tattaunawar cimma yarjejeniyar saye Bournemouth. (Athletic – subscription required)

 

Advertisement

Ana biyan ɗan wasan Norway Erling Haaland, mai shekara 22, £865,000-a kowanne mako a Manchester City. (Mail)

 

Advertisement

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya musanta rade-radin cewa zai bar Haaland ya tafi Real Madrid. (Mirror)

 

Advertisement

Mai rike da kofin Championship Sheffield United ta matsu ta saye ɗan wasan Scotland mai buga gaba Bobby Wales, mai shekara 17. (Football Insider)

 

Advertisement

Mataimakin shugaban kungiyar Barcelona ya gargadi kungiyar kan kudaden da ake kashewa, yana mai cewa ba za su dawo daidai ba sai sun rabu da wasu ‘yan wasa irinsu Gerard Pique, mai shekara 35 da Jordi Alba, ɗan shekara 33, da ɗan wasan tsakiya Sergio Busquets, mai shekara 34. (Mail)

 

Advertisement

Tsohon ɗan wasa Rio Ferdinand ya bukaci Manchester United ta saye ɗan wasan Borussia Dortmund asalin Ingila Jude Bellingham, mai shekara 19, da Real Madrid da Liverpool ke hari. (Mirror)

 

Advertisement

Kocin Leicester City Brendan Rodgers ya bayyana cewa ya yi watsi da tayin da aka gabatar masa har sau biyu na komawa wasu kungiyoyin. (LeicestershireLive)

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending