News
Gwamnatin Kogi ta yi ikirarin mallakar kamfanin siminti na Obajana kuma ta fara yunkurin ƙwato shi daga hannun Dangote
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
A ranar Alhamis ne gwamnatin Kogi ta fara ɗaukar gaɓaran ƙwato kamfanin siminti na Obajana daga hannun kamfanin siminti na Dangote.
Kudurin gwamnatin na kunshe ne a cikin rahoton kwamitin kwararru na musamman don tabbatar da halascin mallakar kamfanin siminti na Obajana zuwa na Dangote.
Saba Dokokin Hanya: Kotu Ta Hukunta Mutum 35 A Edo
Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya rawaito cewa an mika cikakken rahoton ga gwamna Yahaya Bello na Kogi a watan Satumba.
Sakatariyar gwamnatin jihar (SSG), Folashade Ayoade ce ta gabatar da rahoton a ranar Alhamis a Lokoja.
Ayoade ta ce, ” ƙwato kamfanin siminti na Obajana Plc daga kamfanin Dangote Cement Company Limited ya zama wajibi a wannan lokaci.”
SSG ɗin ta gabatar da takardu cewa maida Obajana zuwa ga kamfanin Dangote “Ba halastacce ba, kuma rusasshe ne”.
Ta bayyana cewa a cikin rahoton, an nuna yadda a ka yi amfani da amfani da takaddun mallaka guda 3 na Kamfanin Simintin Obajana, mallakin gwamnatin Jihar Kogi, inda Dangote ya yi amfani da hakan ya ciyo bashin Naira biliyan 63bn.
A cewarta, kwamitin bisa ga binciken da ya gudanar, ya bayar da shawarar cewa jihar Kogi ta dauki matakin kwato kamfanin siminti na Obajana daga hannun Dangote.
