Connect with us

News

Rikicin Boko Haram ya yi sanadin rayuka 100,000 tare da asarar naira tiriliyan 3.24

Published

on

Janar Lucky Irabor
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Babban hafsan tsaro na Najeriya Janar Lucky Irabor,ya ce rikicin Boko Haram ya yi sanadin mutuwar mutum 100,000, yayin da ya raba mutum miliyan biyu da muhallansu tare kuma da janyo hasarar kusan naira tiriliyan 3.24.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito mista Iroba na fadin haka a ranar Talata a lokacin rufe bikin bitar ayyukan ministocin kasar da aka gudanar a Abuja babban birnin kasar.

Advertisement

Kwanturolan Kwastam Ya Yanke Jiki Ya Mutu A Filin Jirgi A Kano

Ya kuma tabbatar da cewa hukumomin sojin kasar sun karbi naria tiriliyan 2.5 a kasasfin kudi na shekaru bakwai da suka gabata, amma duk da haka sun yi kokarin inganta ayyukan harkokin tsaron cikin gida.

Advertisement

Sai dai kuma ya nuna nadama kan kudin da aka ware wa hukumomin sojin kasar, wanda ya ce kashi 35 ne cikin 100 na abin da hukumomin ke bukata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending