News
Kotu ta soke zaɓukan fitar da gwanin APC a jihar Rivers .
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Fatakwal babban birnin jihar Ribas ya soke zaɓukan fitar da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a faɗin jihar, sakamakon cire sunayen wasu daga cikin deliget a zaɓukan fitar da gwanin da jam’iyyar ta gudanar.
Kotun ta yanke hukuncin ne bayan da wasu daga cikin mambobin jam’iyyar suka shigar da ƙara, kan ƙorafin cire sunayensu a matsayin deliget
INEC ta saka ranar gudanar da zaɓuka a jihohin Bayelsa, da Imo, da Kogi
Kotun ta ce ta soke zaɓukan kuma duk mutanen da jam’iyyar ta zaɓa a lokacin zaɓen fitar da gwanin ba halastattun ‘yan takara ba ne.
A lokacin zaɓukan fitar da gwani da jam’iyyar ta gudanar, wasu ‘yan jam’iyyar sun yi zargin cewa an cire sunayensu daga jerin sunayen deliget na jam’iyyar, lamarin da ya sanya su gudanar da zanga-zanga a harabar sakatiyar jam’iyyar da ke birnin Fatakwal.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
