News
Sojoji sun tarwatsa masu zanga-zanga a Sudan
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Sojoji a Kasar Sudan sun watsa hayaki mai sa hawaye a ƙoƙarin hana dubban masu zanga zanga maci zuwa fadar shugaban kasa.
Likitoci sun ce mutum ɗaya ya mutu bayan da motar sojojin ta buge shi.
INEC ta saka ranar gudanar da zaɓuka a jihohin Bayelsa, da Imo, da Kogi
Ana boren ne a duka faɗin Sudan, domin tunawa da juyin mulkin da ya toshe kafar dawowa mulkin dimokradiyya.
Ana zanga-zanga kusan duk mako a Sudan, tun bayan da Shugaban rundunar sojin kasar Abdel Fattah Al-Burhan ya kwace mulki.
Ana zargin sojojin da kashe sama da masu bore 118 a cikin shekara daya, kuma ƙwace mulkin da sojoji suka yi, ya sa ƙungiyoyin bayar da agaji sun yanke kai taimako zuwa ƙasar, duk da halin matsin tattalin arziki da ta ke ciki.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
