Connect with us

News

ECOWAS Ta Bukuci A Gudanar Da Sahihin Zaben 2023 A Najeriya 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS ta roki hukumomin Najeriya da su tashi tsaye, wajen ganin kasar ta gudanar da karbaben zabe a shekara mai zuwa saboda muhimmancin ta ga Afirka baki daya.

 

Advertisement

Tawagar kungiyar da ta ziyarci Najeriya domin ganin shirin zaben a karkashin tsohon shugabar hukumar zaben Ghana, Dr Kwadwo Afari-Gyan, ta bayyana haka ne lokacin da ta gana da shugaban hukumar zabe Farfesa Mahmud Yakubu a birnin Abuja.

Sojoji sun tarwatsa masu zanga-zanga a Sudan

Advertisement

Shugaban bangaren siyasa na kungiyar ECOWAS, Dr Remi Ajibewa yace sun ziyarci Najeriya ne domin ganin yadda shirin zaben ke gudana kamar yadda dokar kungiyar ta tanada.

 

Advertisement

Ajibewa yace kudurorin kungiyar sashe na 11 da 12 da na 13 sun baiwa kungiyar damar tura jami’an sa ido kowacce kasa dake yankin duk lokacin da za’a gudanar da zaben shugaban kasa.

 

Advertisement

Saboda haka jami’in yace ziyarar da suka kai Najeriya ba itace ta farko ba, domin duk lokacin da za’a gudanar da zabe sukan yi haka.

 

Advertisement

Daraktan yace ECOWAS ta bayyana fatan ganin zaben na shekara mai zuwa ya gudana ba tare da matsala ba, saboda irin jagorancin da Najeriya ke bayarwa a yankin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending