Connect with us

News

‘Ku karbi kudi idan an ba ku a lokacin zabe amma ku zabi cancanta’

Published

on

Yayin da babban zabe a Najeriya ke tafe, wasu ‘yan siyasa a kasar sun ce ba laifi bane masu kada kuri’a su karbi kudi idan an basu a lokacin zabe, amma kuma su zabi cancanta.

 

Advertisement

‘Yan siyasar sun bayyana hakan ne a yayin da wasu masana da kungiyoyin kare dimokradiyya ke fargabar cewar siyasar kudi musamman sayen kuri’u na iya mamaye babban zaben kasar da ke tafe.

Shugaban Jamus da na Faransa za su gana kan tsamin dangantakar kasashen .

Advertisement

Hon Yusuf Umar Garkuwa, matashin ɗan siyasa ne daga jihar Kaduna, ya shaida wa BBC cewa, ba bu laifi masu zaɓe su karɓi kuɗi, tun da ko sun karɓa ba wanda zai tilasta musu zaɓen wanda ba sa ra’ayi.

 

Advertisement

Ya ce ya na ganin hakan zai magance matsalar siyasar kuɗi gaba ɗaya a Najeriya.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hon Yusuf Umar Garkuwa, ya ce “ Shi zabe abu ne da za ayi shi a boye, don haka don mutum ya baka kudi ka zabe shi bai isa ya bika akwatin zabe don ganin abin da zaka zaba ba.”

 

Advertisement

 

Saboda haka ka amshi kudin, amma kuma ka zabi abin da ya dace in ji shi.

Advertisement

 

Ya ce idan har ‘yan siyasa na bayar da kudi ana karba kuma ba a zabensu, ai gobe ba zaka fito ka kara bayar da kudi don a zabe ka ba.

Advertisement

 

Kuma idan ma ka ga wani zai bayar da kudi don a zabe shi ai zaka bashi shawara a kan kada ya soma don kai ma kayi baka ji dadi ba in ji shi.

Advertisement

 

Hon Yusuf Umar Garkuwa, ya ce idan har ana yin haka to a iya samun sauki a siyasar kudin da ake a Najeriya.

Advertisement

 

Matashin dan siyasar ya ce, ‘‘Idan har ana wayar wa mutane kai a kan ‘yancinsu, da kuma zabar cancanta, za a rinka samun sauki a siyasar kudi, domin mutane za su karbi kudin dan takara amma kuma su zabi abin da suke so.”

Advertisement

 

Ya ce ba wai siyasar kudi ba zata yi tasiri a zaben mai zuwa ba, zata yi a wasu wuraren, amma ba a ko ina ba, don haka in da zata yi tasirin ma yakamata mutane su gane ‘yancinsu na shekara hudu suke sayarwa.

Advertisement

 

Hon Yusuf Umar Garkuwa, ya ce akwai wasu ‘yan takarar da basu da abin da zasu fada a zabe su ko kuma su nuna, don haka dole su fito da kudi a lokacin zabe saboda akwai talauci da yunwa da ke addabar mutane.

Advertisement

 

Ya ce don haka ku karba ku cinye ku zabi wanda kuke ganin ya fi cancanta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending