Sports
Kenya ta bukaci FIFA ta janye dakatarwar da ta yi mata a harkar tamaula
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Kenya ta bukaci hukumar kwallon kafa ta duniya ta janye dakatarwar da ta yi mata daga shiga harkar tamaula.
A watan Fabrairu ne FIFA ta dakatar da Kenya saboda zargin karkatar da kudade da ake zargin wasu shugabannin hukumar kwallon kafar kasar da yi.
COP 27: Ambaliyar Ruwa A Najeriya, Da Wasu Ya Zama Wani Bangare Na Abun Tattaunaw
To amma a yanzu gwamnatin ta rubuta wa FIFA cewa ta rusa hukumar ta FKF kamar yadda aka shardanta, a don haka tana bukatar a maido ta harkar tamaula.
Dakatarwar da FIFA ta yi wa Kenya ta kawo mata a cikas, bayan da aka hana ta shiga wasannin share fagen zuwa gasar cin kofin Afrika mai zuwa a duka tawagar mata da ta maza.
Advertisements
