Sports
Gerrard Pique Ya Yi Ritaya Daga Kwallon Kafa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona, Gerrard Pique, ya ce wasan da kungiyarsa za ta yi da Almeria a ranar Asabar shi ne wasansa na karshe a filin wasa na Camp Nou.
Dan wasan ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter a ranar Alhamis.
Ƴan Nijeriya ba su da hujjar da za su yi kukan yunwa, in ji Buhari
Ya shaida cewar wasan da Barcelona za ta yi a ranar Asabar shi ne na karshe dai zai yi da kungiyar a gida, kafin a fara Gasar Kofin Duniya.
Bayan yanke hukuncin dan wasan, Barcelona za ta warware kwantaragin da ta kulla da shi wanda zai kare a karshen kakar wasanni ta bana.
Pique ya buga wasanni 573, sannan ya zura kwallo 57 a raga a rayuwarsa ta kwallon kafa.
Dan wasan ya kuma lashe kofi 36 a matsayin dan wasan bayan Barcelona.
