News
Sojoji Sun Kashe Jagororin IPOB 13
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Sojojin Najeriya sun kashe wasu kwamandoji 13 na kungiyar ta’addanci ta IPOB a yankin Kudu maso Gabas.
Dakarun sun kuma cafke bokan IPOB tare da wasu ’yan kungiyar su biyar, inda suka kwato na’urar rajistar masu zabe a yayin zagargazar da suke ci gaba da yi wa ’yan ta’addan a yankin.
Daraktan Yada Labarai na Rundunar Tsaro ta Najeriya, Birgediya-Janar Musa Danmadami, ya ce, “A mako guda mun kashe jagororin IPOB 13, muka cafke wasu shida, ciki har da bokan kungiyar kamar yanda jaridar Aminiya ta rawaito
“Mun kwato bindigogi 15 da albarusai iri-iri da kuma kaki da sauran kayayyakin soji a hannunsu.
“Sauran sun hada da akwatin zabe da na’urar rajistar masu zabe na Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da na’urorin sadarwa da motoci da sauransu.”
Birgediya-Janar Musa Danmadami ya ce tuni sojojin suka mika ’yan ta’addan na IPOB da kayayyakin da aka kwace a hannunsu ga hukumomin da suka dace domin gurfanar da su a kotu, saboda su girbi abin da suka shuka
