Connect with us

News

Kotu Ta Tabbatar Da Hukuncin Hana PDP Shiga Takarar Gwamna A Zamfara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Jihar Sakkwato, ta tabbatar da hukuncin hana dan takarar Gwamnan PDP a Jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare shiga zaben 2023.

 

Advertisement

Wannan na zuwa ne bayan da kotun ta yi fatali da karar da jam’iyyar da kuma dan takarar suka shiga suna masu neman halascin shiga zaben na badi.

Buhari zai tafi Nijar taron ƙolin ƙasashen Afirk

 

Advertisement

Kwamishinan Yada Labarai Jihar Zamfara, Ibrahim Magaji Dosara ne ya bayyana hukunci kotun cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

 

Advertisement

A cewar sanarwar, “daukaka karar ya saba wa hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Gusau ta yanke a ranar 16 ga watan Nuwamba 2022, wanda ya soke zaben fid-da-gwanin dan takarar gwamna na jam’iyyar saboda rashin bin ka’idar Dokar Zabe ta 2022 da ka’idojin PDP.

 

Advertisement

“A cikin hukuncin wanda alkalai uku na Kotun Daukaka Kara suka yanke, Mai Shari’a M L Shuaibu JCA, Shugaban Kotun Daukaka Kara ta Sakkwato, wanda ya zartar da hukuncin, ya ce daukaka karar aiki ne na ilimi.

 

Advertisement

Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda haka, an yi watsi da karar sannan wadanda suka gabatar da karar za su biya tarar naira dubu 100.”

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending