Connect with us

News

Tinubu ya taya Atiku murnar cika shekara 76 da haihuwa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Ɗan takarar jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya abokin hamayyarsa na PDP Atiku Abubakar murnar cika shekara 76 da haihuwa.

Advertisement

Doka ta hana ɗan takarar shugaban ƙasa ya kashe sama da Naira biliyan 500 — INEC

A yau Juma’a ne tsohon mataimakin shugaban ƙasar kuma haifaffen Jihar Adamawa da ke arewacin ƙasar ya yi bikin zagayowar ranar haihuwar tasa.

“Ina taya Atiku Abubakar murnar ranar haihuwarsa ta 76,” in ji Tinubu cikin wani saƙon Twitter. “Ina yi masa fatan alheri.”

Advertisement

Wannan ne karo na shida da Atiku zai yi takarar shugaban ƙasa bayan ya yi rashin nasara a 1993, da 2007, 2011, da 2015, da kuma 2019.

A ranar 25 ga watan Fabarairu mutanen biyu za su fafata a babban zaɓen da ‘yan Najeriya za su zaɓi shugaban ƙasa da gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da na tarayya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending