News
Tinubu ya taya Atiku murnar cika shekara 76 da haihuwa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ɗan takarar jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya abokin hamayyarsa na PDP Atiku Abubakar murnar cika shekara 76 da haihuwa.
Doka ta hana ɗan takarar shugaban ƙasa ya kashe sama da Naira biliyan 500 — INEC
A yau Juma’a ne tsohon mataimakin shugaban ƙasar kuma haifaffen Jihar Adamawa da ke arewacin ƙasar ya yi bikin zagayowar ranar haihuwar tasa.
“Ina taya Atiku Abubakar murnar ranar haihuwarsa ta 76,” in ji Tinubu cikin wani saƙon Twitter. “Ina yi masa fatan alheri.”
Wannan ne karo na shida da Atiku zai yi takarar shugaban ƙasa bayan ya yi rashin nasara a 1993, da 2007, 2011, da 2015, da kuma 2019.
A ranar 25 ga watan Fabarairu mutanen biyu za su fafata a babban zaɓen da ‘yan Najeriya za su zaɓi shugaban ƙasa da gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da na tarayya.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
