Connect with us

News

An bai wa Majalisar Kano shawarar hukunci mai tsanani wajen kafa dokar haƙƙin yara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

A ranar Alhamis Majalisar Dokokin Jihar Kano a arewacin Najeriya ta yi zama don sauraron ra’ayoyin jama’a a kan yunkurin kafa dokar kiyaye haƙƙin ƙananan yara.

 

Advertisement

Mahukunta da sauran masu ruwa da tsaki a harkar kiyaye hakkokin yara sun ba da shawarar a yi tanadin hukunci mai tsanani ga masu tauye haƙƙin yaran, ciki har da ɗaurin shekara bakwai da tara mai yawa ga masu cin zarafin su.

Tsohon shugaban jami’ar Gusau zai sha ɗaurin shekara 35

Majalisar Kanon ta bayyana cewa suna yunkurin kafa dokar ne saboda a hukunta masu kuntata musu, kuma wannan ne ya sa aka yi tanadin hukunce-hukunce daban-daban.

Advertisement

 

Mataimakin Kakakin Majalisa Kabiru Hassan Dashi – kuma shugaban kwamitin harkokin mata da walwalar jama’a – ya faɗa wa BBC Hausa cewa dokar za ta ba da dama agina wa marayu gidaje da ɗaukar nauyin karatunsu.

Advertisement

 

Ya ƙara da cewa wannan ne zama na ƙarshe da suka yi kafin amincewa da dokar a Majalisa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending