Connect with us

News

Ba za mu ƙara kuɗin man fetur ba a yanzu – Gwamnatin Najeriya

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da niyyar ƙara kuɗin man fetur “a wannan lokaci” yayin da ‘yan ƙasar ke ci gaba da fama da dogayen layi a gidajen man.

Advertisement

 

Wata sanarwa da hukumar kula da rarraba fetur ta NMDPA ta fitar ta ce ya zama dole su musanta jita-jitar da ake yi game da farashin man da kuma ƙarancinsa a cikin Najeriya.

Advertisement

Ina fargabar sakamakon zaɓen 2023 – Jega

Sanarwar ta ce kamfanin mai na Najeriya, NNPC Limited, ya tanadi man fetur da zai isa amfanin ƙasar tsawon kwana 34.

 

Advertisement

“Ana bai wa ‘yan kasuwa da sauran jama’a shawarar su daina fargaba da kuma sayen man don karkatarwa da kuma ɓoye shi,” in ji NMDPR.

 

Advertisement

Bisa al’ada, akan fuskanci ƙarancin man fetur a duk ƙarshen shekara a Najeriya duk da cewa a baya-bayan nan ba a ga hakan ba sakamakon ƙarin kuɗin man da gwamnati ta dinga yi akai-akai.

 

Advertisement

Sai dai wannan karon an fara ƙarancin fetur ɗin tun daga tsakiyar 2022, inda wasu gidajen mai ke sayar da lita ɗaya kan N200 zuwa N250 maimakon N185 farashin gwamnati.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending