News
Kongo ta ba da hutun zaman makoki na ƙasa kan kisan kiyashi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaban Congo ya sanar da hutun kwanaki uku a matsayin na zaman makoki kan kisan kiyashin da aka yi a gabashin ƙasar.An daɗe ba a samu irin wannan rikicin ba a yankin da lamarin ya faru amma Shugaba Feliz Tshisekedi ya bayyana cewa sama da mutum ɗari ne aka kashe a ƙauyen Kishi-she.
Wakiliyar BBC ta ce gwamnatin ƙasar ta ɗora alhakin kisan kan ƴan tawayen M23, duk da cewa sun musanta zargin.
Netherlands ta tsallaka mataki na gaba bayan doke Amurka da ci 3-1 a Qatar
An ta samun ƙarin rikice-rikice tun bayan da Jamhuriyyar Congo da Rwanda suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a makon da ya gabata.
Congo da Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya duk sun zargi Rwanda da goyon bayan yan tawayen M23 duk da cewa Rwandan ta musanta hakan.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
