Connect with us

News

Kongo ta ba da hutun zaman makoki na ƙasa kan kisan kiyashi

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

Shugaban Congo ya sanar da hutun kwanaki uku a matsayin na zaman makoki kan kisan kiyashin da aka yi a gabashin ƙasar.An daɗe ba a samu irin wannan rikicin ba a yankin da lamarin ya faru amma Shugaba Feliz Tshisekedi ya bayyana cewa sama da mutum ɗari ne aka kashe a ƙauyen Kishi-she.

 

Advertisement

Wakiliyar BBC ta ce gwamnatin ƙasar ta ɗora alhakin kisan kan ƴan tawayen M23, duk da cewa sun musanta zargin.

Netherlands ta tsallaka mataki na gaba bayan doke Amurka da ci 3-1 a Qatar

An ta samun ƙarin rikice-rikice tun bayan da Jamhuriyyar Congo da Rwanda suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a makon da ya gabata.

 

Congo da Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya duk sun zargi Rwanda da goyon bayan yan tawayen M23 duk da cewa Rwandan ta musanta hakan.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending