Connect with us

News

Budurwa ta kai ƙarar saurayinta Kotu kan yaɗa tsiraicinta a Facebook

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Wata budurwa a Kano ta maka saurayinta a kotun Shari’ar Musulunci kan barazanar yada hoton tsiraicinta a Facebook.

Advertisement

 

’Yan sanda sun gurfanar da matashin a gaban kotun mai shari’a Nura Yusuf Ahmad, da ke unguwar Gama PRP a Karamar Hukumar Nassarawa, bisa tuhumar tsoratarwa.

Advertisement

’Yan wasan Kamaru 32 sun gaza tsallake gwajin shekarun ‘yan ƙasa da 17

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, mai gabatar da karar, Aliyul ‘Abidin, ya shaida wa kotun cewa budurwar ta janye sakamakon wanda ta shigar da karar a kansa saurayinta ne.

 

Advertisement

An zargi matashin da yunkurin bata wa budurwa suna, bayan ya yi mata barazanar yada hoton tsiraicinta a Facebook, wanda hakan na iya bata mata suna.

 

Advertisement

Tun da farko saurayin ya yi wa budurwar barazana ne domin ta saya masa waya.

 

Advertisement

Sai dai bayan janye kararta, kotun ta sallami matashin da ake tuhuma, inda ta gargade shi kan yi wa mutum barazana.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending