Connect with us

News

Mutum 25 Sun Mutu A Yayin Da Sabuwar Mugunyar Cuta Ta Bulla A Kano. 

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

A kalla mutane 15 ne suka rasu sakamakon abin da ake zargi cutar diptheria ne a jihar Kano zuwa ranar 18 ga watan Janairu, a cewar Dr Abdullahi Kauran-Mata, masanin cututtuka masu yaduwa.

Advertisement

 

Ya ce an samu mutum 78 masu dauke da cutar mai gaggawar yaduwa a kananan hukumomi 14 na jihar.

Advertisement

Sadakin Aure Kadai Za Mu Mayar — Lauyan Balaraba Ganduje

Kauran-Mata ya fada wa kamfanin dillancin labarai NAN, a ranar Alhamis a Abuja, cewa an dauki samfuri guda 27 an kai su dakin gwaji, an tabbatar da takwas kuma mutane uku sun mutu a jihar.

 

Advertisement

Ya ce: “A halin yanzu gwamnatin jiha ta kafa cibiyar kula da masu diphtheria da tallafi daga kungiyoyin tallafawa al’umma na Médecins Sans Frontières (MSF) a asibitin kwararru na Murtala Muhammad inda ake kula da masu dauke da cutar.

 

Advertisement

“An kuma fara sanarwa a gidajen radio tare da tattaunawa kan cutar. “Gwamnatin jihar ta kuma kafa tawaga mai kula da yaduwar cutar karkashin jagorancin jami’in kula da bullar annoba don saka ido.”

 

Advertisement

Kauran-mata ya ce ana iya kare kamuwa da diptheria ta hanyar rigakafi.

 

Advertisement

A cewarsa: “Amma, kananan yara ake yi wa rigakafin karkashin tsarin riga kafi na kasa.

 

Advertisement

Sauran hanyoyin kare kai daga kamuwa sun hada da saka takunkumin fuska, wanke hannu da tsafta, takaita taba wadanda suka kamu da kai su asibiti cikin gaggawa.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending