Connect with us

News

Mazauna Karkara Na Cikin Kunci Saboda Karancin Sabbin Takardun Kudi’

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wani dan kasuwa da ke garin Saminaka a Jihar Kaduna, Alhaji Hamisu Rabi’u Mai Manja Saminaka, ya bayyana cewa talakawan da ke zaune a kauyukan kasar nan, a halin yanzu suna cikin wani mawuyacin hali, sakamakon rashin ganin sababbin takardun kudaden da aka sauyawa fasali.

 

Advertisement

Alhaji Mai Manja ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da Aminiya a ranar Lahadin nan.

 

Advertisement

Halaand yaci gaba da kafa tarihi a gasar Premier

Ya ce “yanzu ko manyan garuruwa ka shiga, babu sababbin kudaden nan, balle kuma ka shiga kauyuka.

 

Advertisement

“Wannan matsala ta shafi kowa a Najeriya, talakawa da masu kudi.

“An ce mutane su daina karbar tsofaffin kudade, kuma babu sababbin kudaden.

Advertisement

 

“Don haka yanzu harkokin kasuwanci sun fara tsayawa a kauyukan kasar nan.

Advertisement

 

“Domin idan ’yan kasuwa suka karbi tsofaffin kudaden nan, suka kai banki ba a karba.

Advertisement

 

“Mutane sun fito da tsofaffin kudade daga ko’ina a kauyukan kasar nan.Kuma ga shi babu sababbin kudaden.

Advertisement

 

 

Advertisement

“Yanzu ko kudin da mutanen kauye za su yi cefane su kai wa iyalansu babu.

 

Advertisement

“Don haka ina kira ga Shugaban Kasa da Gwamnan Babban Bankin Najeriya, su dubi halin da talakawa suka shiga, su kara wa’adin karbar tsofaffin kudaden nan.

 

Advertisement

“Ina kuma rokon da su dauki matakan samar da sababbin kudaden a ko’ina a kasar nan.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending